31 Yuli 2018 - 17:10
Wata Kotu A Kaduna Ta Sallami Shari'ar 'Yan Shi'a

Babbar kotun jihar Kaduna a yau Talata 31 ga Yuli, 2018 ta zartar da hukuncin da ya faranta mana wanda Lauyoyinmu suka shigar “No Case Submission ” dangane da ‘yan’uwa musulmi kusan 100 da suke tsare suna fuskantar tuhumar kisa tun bayan kisan kiyashin da aka yi mana a Zariya a Disamban 2015.

Yau dai kotu ta wanke su tare da sallamar su.

Kamar yadda aka sani cewa, yau talata(31/7/2018)ne High court 6 dake kaduna ta sanya domin yanke hukunci game da case din ‘yan,uwa da akeyi a kotun wadanda jami,an tsaro suka kama a waqi,ar zaria ta 2015.

A hukuncin na kotun, ta wanke ‘yan,uwa tace basu aikata laifi ba, ta kuma tace, a sakesu nan take ba tare da bata lokaci ba.

A yanzu haka, ‘yan,uwa dai sun wuce prison don su kwaso kayayyakinsu. Allah na tare da muminai.